DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tabarbarewar tsaro ba ta da alaka da gazawar jami’an tsaro sai dai siyasantar da matsalar – Rabi’u Kwankwaso

-

Jagoran Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce tabarbarewar tsaro a Nijeriya ba gazawar sojoji ba ce, illa dai rashin ƙwazon shugabannin siyasa.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a Kano yayin ƙaddamar da rundunar Kano State Neighbourhood Watch Corps da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa, inda aka gabatar da jami’ai 2,000 da aka horas domin taimakawa tsaron al’umma.

Google search engine

A cewarsa, sojojin Nijeriya jajirtattu ne kuma kwararru, amma abin da aka rasa shi ne ƙwazon siyasa, musamman daga Babban Kwamandan Rundunonin Tsaro, yana mai jaddada cewa gwamnati ta samar da kayan aiki, makamai da horo ga jami’an tsaro.

Tsohon Ministan Tsaron ya kuma yaba wa gwamnatin Kano kan kafa rundunar tsaron unguwanni, yana mai cewa mataki ne da ya dace domin fuskantar ƙalubalen tsaro, musamman a yankunan iyaka da makwabtan jihohin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mawaki Davido ya koma jam’iyyar Accord Party, inda kawunsa Gwamnan Osun Adeleke ya koma

Mawaki Davido, ya sanar da shirin sa na shiga jam’iyyar Accord, inda zai bi sawun kawunsa, Gwamna Ademola Adeleke na Osun. Mawakin ya ce zai kasance...

Shugaba Tinubu ya nuna jarumta wajen aiwatar da tsare-tsare masu wahala a 2025 – Jam’iyyar APC

Jam’iyyar APC ta ce Shugaba Bola Tinubu ya nuna jarumtaka ta musamman da jajircewa wajen tafiyar da Nijeriya cikin sauye-sauyen tattalin arziki da na gwamnati...

Mafi Shahara