DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta umarci a duba tare da sake fitar da dokokin haraji

-

Majalisar Wakilai a Nijeriya ta ce ta fara duba dokokin gyaran haraji bayan korafe-korafen jama’a da zargin an sauya wasu sassan dokokin da aka riga aka wallafa a sanarwar da gwamnati ta ba jama’a.

 

Google search engine

Mai magana da yawun Majalisar Akin Rotimi, ya ce an kafa kwamitin da zai binciki yadda aka bi wajen tsara wa da kuma aiwatar da dokokin domin gano ko akwai kura-kurai, tangarɗa ko wani tsoma baki a tsarin majalisa da na gudanarwa.

 

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito Rotimi ya ƙara da cewa Majalisar ta umarci Akawun Majalisar a sake wallafa dokokin tare da fitar da sahihan kwafi-kwafi na abin da Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai suka amince da shi.

 

Wannan mataki ya biyo bayan zargin da ɗan majalisa Abdussamad Dasuki daga Sokoto ya yi cewa dokokin da aka wallafa sun bambanta da waɗanda aka tattauna kuma aka amince da su.

 

Lamarin da ya sa ƙungiyoyi da jam’iyyun adawa, da ma kungiyoyi irin su NLC da NBA na neman a dakatar da aiwatar da dokokin da aka shirya su fara aiki daga ranar 1 ga watan Janairu na 2026, duk da karewar da Gwamnatin Tarayya ke yi cewa dokokin za su inganta tsarin haraji da rage nauyi ga marasa ƙarfi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara