Sakataren Gwamnatin Nijeriya (SGF), Sanata George Akume, ya auri Sarauniya Zaynab Ngohemba, tsohuwar matar Ooni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi.
Jaridar Punch ta ce an bayyana hakan ne a ranar Juma’a ta hannun wani mamba na iyalan Dajoh, Abraham Double-d Dajoh, ta shafin Facebook.
Iyalan Dajoh sun tabbatar da auren tare da tarbar Sarauniya Zaynab a hukumance zuwa gidan iyali da ke Mbakor, Jihar Benue, a wannan watan Disamba.



