DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ne ya sahale wa Amurka kai hari bayan Nijeriya ta ba da bayanan sirri – Gwamnati

-

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya amince a kai hare-haren sama da Amurka ta yi kan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

 

Google search engine

Ministan Harkokin Waje Yusuf Tuggar ya ce hare-haren hadin gwiwa ne tsakanin kasashen biyu, inda Najeriya ta bayar da muhimman bayanan sirri kuma an aiwatar da su ne bayan samun cikakkiyar amincewar shugaban kasa.

 

Tuggar ya jaddada cewa aikin bai sabawa ikon kasa ba kuma ba ya da nasaba da addini.

 

Gidan talabijin na Channels ya ambato shi ya ce Najeriya kasa ce mai addinai da dama kuma ta na hada gwiwa da abokan hulda irinsu Amurka ne domin yaki da ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

 

A cewar Amurka, an kashe ‘yan ISIS da dama a hare-haren, yayin da AFRICOM ta tabbatar da cewa an yi su ne tare da cikakken hadin kai da hukumomin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara