DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar EFF ta Afirka ta Kudu ta yi tir da amincewar Nijeriya kan harin Amurka

-

Jam’iyyar Afirka ta Kudu ta dan gwagwarmayar adawa da Turawa Julius Malema (EFF) ta yi Allawadai da yadda Nijeriya ta amince da harin Amurka a cikin kasar kan ‘yan ta’adda.

 

Google search engine

A cikin wata sanarwa, EFF ta nuna damuwa cewa Najeriya ba ta kalubalanci matakin na Amurka ba, tana gargadin cewa irin wannan yarda na iya zama wani abu mai haɗari da ka jaddada cewa gwamnatocin Afirka ba sa iya kare kansu daga matsin lambar ƙasashen waje.

 

Haka kuma EFF ta dage kan cewa wannan mataki na gwamnati na iya buɗe ƙofa ga tsoma bakin ƙasashen waje a nahiyar Afirka nan gaba.

 

Sai dai gwamnatin Najeriya ta kare kanta, tana mai cewa an amince da kaddamar da harin ne bayan tattara bayanai na sirri da kuma tsara dabarun aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara