DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwankwaso ya umurci a ba ’ya’yan ’yan majalisar Kano da suka rasu tikitin takarar maye gurbinsu

-

Jagoran darikar Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya umarci a bai wa ‘ya’yan ‘yan majalisar dokokin jihar Kano guda biyu da suka rasu damar tsayawa takara a karkashin jam’iyyar NNPP domin maye gurbin iyayensu.

 

Google search engine

Cikin wata tattaunawa da DCL Hausa ta yi da shugaban jam’iyyar NNPP na Kano Dr Hashim Sulaiman Dungurawa, ya tabbatar da cewa an cimma matsayar ne bayan da Kwankwaso ya gana da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da kuma iyalan mamatan a gidansa da ke Kano.

 

A cewar sa, amince musu su tsaya takarar don wakiltar kananan hukumomin Ungoggo da Municipal a zauren majalisar dokokin Kano, ya zo ne duba da irin gudunmawar da iyayensu suka bayar wajen hidimtawa al’umma.

 

Dungurawa ya ce suna kyautata zato tare da sa ran cewa Sa’ad Aminu Sa’ad, da kuma Nabil Aliyu Daneji za su kwatanta irin rawar da iyayensu suka taka a fagen siyasa da kuma aikin hidimtawa al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara