DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun nemi taimakon Turkiyya wajen yakar matsalar tsaro a Nijeriya – Shugaba Tinubu

-

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa ta nemi taimakon kasar Turkiyya wajen yakar matsalar tsaro da ke addabar wasu sassan Nijeriya.

 

Google search engine

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Juma’a yayin tattaunawa da wata tawagar kungiyar Kiristoci ta Nijeriya a gidansa da ke jihar Legas.

 

Sanarwar da hadiminsa Bayo Onanuga ya fitar, ta ce ya bukaci samun hadin kai daga kungiyar, musamman wajen hakuri da kuma fahimtar irin matakan da gwamnatinsa ke dauka.

 

Kazalika ya jaddada kudurin kafa ‘yansandan jihohi, a daidai lokacin da gwamnati ke kan aikin hadin gwiwa da kasar Amurka wajen yakar matsalar tsaro, kamar yadda Channels TV ya wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara