Ministan Abuja Nyesom Wike ya bayyana cewa shi ne dan siyasa na biyu da aka fi ci wa zarafi a Nijeriya bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.
Wike ya bayyana haka ne a garinsa na Ochiba da ke karamar hukumar Ahoada ta gabas a jihar Rivers, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Wike dai ya jaddada ci gaba da goyawa shugaba Tinubu baya a kowane lokaci, tare da cewa daga watan Janairun 2026, za a sake komawa siyasa a jihar Rivers a hukumance.



