DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Zamfara zai yi karin albashi ga Malaman Addini

-

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya sanar da shirin ƙara albashi ga limaman Juma’a 11,300 da malaman addinin Musulunci a faɗin jihar, inda sabon tsarin zai fara aiki daga Janairu 2026.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya ke ganawa da Malaman addini.

Google search engine

Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta walwala da yanayin malamai da limamai a jihar.

A cewarsa, gwamnatin jihar na kashe Naira miliyan 81.8 a kowane wata wajen biyan alawus-alawus ga limamai, malamai da masu tsaftace masallatai.

Ya ce shirin ya biyo bayan shawarar kwamitin da gwamnan ya nada inda ya ba da shawarar a kara albashinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban layin wutar lantarkin Nijeriya National Grid ya fadi

Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya fadi Litinin din nan, lamarin da ya jefa ’yan Nijeriya da dama cikin duhu bayan da manyan tashoshin...

‘Yan bindiga sun kai hari a wani kauye na jihar Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari a kauyen Gebbe da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi, inda rahotanni ke nuna an rasa rayuka yayin da...

Mafi Shahara