DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu asarar rayuwa bayan fashewar wani abu a asibitin Bagudo ta Kebbi – Ƴan sandan Nijeriya

-

Rundunar ’yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da fashewar wani abu a babban Asibitin Bagudo da ke karamar hukumar Bagudo ta jihar a Talatar nan.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sanda ta jihar SP Bashir Usman ya fitar a Birnin Kebbi, inda ya tabbatar cewa rundunar ta ƙillace wajen bayan jin ƙarar fashewar da aka da asubahin Talata, 30 ga Disamba, 2025, a harabar asibitin.

Google search engine

Ya ce rundunar tsaro ta hadin gwiwa wacca ta kunshi ’yan sanda, sojoji da jami’an sa-kai ta garzaya wurin cikin gaggawa dan tabbatar da tsaro.

Kazalika ya bayyana cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoton ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbanin faruwar lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabbin dokokin haraji za su fara aiki a 1 ga Janairu 2026 — Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da cewa sabbin dokokin haraji za su fara aiki a ranar 1 ga Janairu, 2026, kamar yadda aka tsara tun da...

An takaita amfani da kafafen sada zumunta a Guinea

Guinea ta takaita amfani da TikTok, YouTube da Facebook yayin jiran sakamakon zaben shugaban kasa. Gwamnatin Guinea ta takaita shiga shafukan sada zumunta na TikTok, YouTube...

Mafi Shahara