DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta tasa keyar Malami, matarsa da dansa gidan yarin Kuje kan zargin badakalar sama da Naira biliyan 8

-

Kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami SAN tare da ɗansa da ɗaya daga cikin matansa a gidan gyaran hali na Kuje.

Mai shari’a Justice Emeka Nwite ne ya bayar da umarnin a ranar Talata, 30 ga Disamba 2025, bayan sauraron hujjoji daga lauyoyin wadanda ake tuhuma karkashin jagorancin Joseph Daudu SAN da kuma lauyan masu gabatar da ƙara na EFCC Ekele Iheneacho SAN.

Google search engine

Malami, tare da ɗansa Abubakar Malami da matarsa Asabe Bashir na fuskantar tuhumar badakalar kuɗi guda 16, wadda hukumar EFCC ta shigar a kansu.

EFCC na zargin cewa wadanda ake tuhumar sun haɗa kai a lokuta daban-daban wajen canza salo na kuɗaɗen da aka samu ta haramtacciyar hanya, waɗanda darajarsu ta kai Naira biliyan 8.7.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabbin dokokin haraji za su fara aiki a 1 ga Janairu 2026 — Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da cewa sabbin dokokin haraji za su fara aiki a ranar 1 ga Janairu, 2026, kamar yadda aka tsara tun da...

An takaita amfani da kafafen sada zumunta a Guinea

Guinea ta takaita amfani da TikTok, YouTube da Facebook yayin jiran sakamakon zaben shugaban kasa. Gwamnatin Guinea ta takaita shiga shafukan sada zumunta na TikTok, YouTube...

Mafi Shahara