Manyan shugabannin jam’iyyar APC sun bayyana cikakken goyon bayansu ga gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, domin neman wa’adi na biyu, duk da rikicin siyasa da ke ƙara tsananta tsakaninsa da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.
Sakataren APC na ƙasa, Ajibola Basiru, ya ce jam’iyyar za ta tsaya tsayin daka wajen kare Fubara a matsayin gwamnan APC, yana mai jaddada cewa yana tafiyar da mulkin jihar yadda ya kamata.
Haka kuma, shugabancin jam’iyyar ya tabbatar da Fubara a matsayin jagoran APC a Rivers.
Sai dai Wike ya ce sauya sheƙar Fubara zuwa APC ba ta ba shi tabbacin tikitin takara kai tsaye ba, yana mai barazanar hana shi dawowa.




Comment:anayi muna gani, fatanmu Allah yakaimu lokaci.