Dakarun 12 Brigade na Sojojin Nijeriya sun yi nasarar kawo karshen ‘yan bindiga uku tare da kama wanda ake zargin mai samar musu da kayayyaki a yayin wani samame a Kabba Bunu da Yagba West a Jihar Kogi.
Aikin ya gudana ne a ranar Asabar 3 ga Janairu, 2026, bayan samun bayanan sirri kan motsin ‘yan bindiga.
Jaridar Punch ta ruwaito Lt. Hassan Abdullahi, na cewa sojojin sun yi musu kwanton-bauna inda aka yi artabu da bayarayin, lamarin da ya tilasta ‘yan bindigar janyewa.



