DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutane fiye da 30 a jihar Neja

-

Aƙalla mutane 30, ciki har da mata, sun rasu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari Kasuwan Daji da ke ƙauyen Demo, Borgu LGA a Jihar Niger, a ranar Asabar.

Maharan sun shiga kasuwar da misalin 4:30 na yamma, inda suka ƙone kasuwar, suka wawashe kayan abinci da sauran dukiyoyi na daruruwan miliyoyin naira, tare da yin garkuwa da wasu mutane.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ambato wani mazaunin yankin ya ce maharan sun fito ne daga dajin National Park a Borgu, kuma sun yi ta’addanci ba tare da wani ƙwakkwaran ƙalubale ba daga jami’an tsaro ba.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Jihar Niger, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da lamarin, yana cewa jami’an tsaro sun ziyarci wurin da safe, inda aka tabbatar da mutuwar sama da 30, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara