Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar kaddamar harin soji kan kasar Colombia, bayan wani farmakin soji da ya kai a Venezuela.
Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya ce yiwuwar kai farmakin soji kan Colombia tunani ne mai kyau,yana zargin gwamnatin kasar da hannu wajen safarar hodar iblis zuwa Amurka.
Trump ya yi wannan furuci ne bayan wani farmaki da sojojin Amurka suka kai a Venezuela, wanda ya janyo cece kuce a duniya tare da tayar da hankula.



