Mataimakin Shugaban NNPP na shiyyar Arewa maso Yamma,Sani Danmasani, ya bayyana cewa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, shi ne jagoran jam’iyyar NNPP, ba Rabiu Musa Kwankwaso ba.
Danmasani ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, inda ya ce bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar NNPP, Gwamna Abba Kabir ne jagoran jam’iyyar kasancewar shi kaɗai ne gwamnan da jam’iyyar ke da shi a halin yanzu.
Jaridar Daily Nigeriyan ta rawaitk Dan Masani ya ce Sanata Rabiu Kwankwaso ya kasance ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a zaɓen 2023 ne kawai, bisa wata yarjejeniya da aka kulla tsakanin jam’iyyar da kungiyar Kwankwasiyya, wadda ta ƙare bayan kammala zaɓen.
Danmasani ya ƙara da cewa wasu manyan mambobin Kwankwasiyya, ciki har da Kwankwaso, an kore su daga jam’iyyar NNPP bisa zargin aikata ayyukan da suka saɓa wa manufofin jam’iyya.



