DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun sace mutane da dama a wasu hare hare da suka kai a Katsina

-

Wasu ’yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hare-hare kan wasu al’ummomi a jihar Katsina, inda suka sace mutane da dama.

Shaidun gani da ido sun shaida wa gidan talabijin na Channels ta wayar tarho a ranar Talata cewa harin ya faru ne a daren Litinin, bayan da ’yan bindigar suka mamaye yankunan, suka kwashe tsawon lokaci suna aikata ta’asa da firgita mazauna wuraren.

Google search engine

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa ’yan bindigar sun fara kai hari a Unguwar Alhaji Barau, daga bisani suka wuce Gidan Dan Mai-gizo da Gidan Hazo, duk a Unguwar Na’alma da ke karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Duk da haka, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba, yayin da har yanzu ba a tantance adadin mutanen da aka kashe ko waɗanda aka sace ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ministan yada labarai ya nesanta kansa da wani rubutu mai taken “Malagi 2027”

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya, Mohammed Idris, ya nesanta kansa daga wani rubutu na siyasa mai taken “Malagi 2027”, wanda...

Wasu tsoffin ‘yan sanda sun roki Tinubu da ya sa a mayar da su aiki bayan tilasta yi musu ritaya

Wasu tsoffin jami’an rundunar ’yan sandan Nijeriya sun sake kira ga rundunar da ta bi hukuncin Kotun Kwadago ta Kasa, wadda ta bayar da umarnin...

Mafi Shahara