DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP za ta gana da Atiku da Peter Obi gabanin zaben 2027 – Emmanuel Ogidi

-

Jam’iyyar PDP ta bayyana shirin ganawa da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, da wasu manyan jiga-jigan siyasa a Nijeriya domin farfado da jam’iyyar.

Shugaban PDP na Kudu maso Kudu, Emmanuel Ogidi ya ce, jam’iyyar ta riga ta ziyarci tsofaffin shugabanni, Olusegun Obasanjo da Ibrahim Babangida, yayin da tana shirin tattaunawa da sauran masu ruwa da tsaki a fagen siyasa, ciki har da Obi da Atiku kamar yadda Channels TV ta ruwaito

Google search engine

A baya-bayan nan, kwamitin gudanarwa na PDP ya gana da tsohon shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, wanda ya tabbatar da kasancewarsa mai cikakken goyon bayan jam’iyyar yayin da PDP ke shirin fuskantar zabuka a Ekiti da Osun, har zuwa zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara