Jam’iyyar PDP ta bayyana shirin ganawa da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, da wasu manyan jiga-jigan siyasa a Nijeriya domin farfado da jam’iyyar.
Shugaban PDP na Kudu maso Kudu, Emmanuel Ogidi ya ce, jam’iyyar ta riga ta ziyarci tsofaffin shugabanni, Olusegun Obasanjo da Ibrahim Babangida, yayin da tana shirin tattaunawa da sauran masu ruwa da tsaki a fagen siyasa, ciki har da Obi da Atiku kamar yadda Channels TV ta ruwaito
A baya-bayan nan, kwamitin gudanarwa na PDP ya gana da tsohon shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, wanda ya tabbatar da kasancewarsa mai cikakken goyon bayan jam’iyyar yayin da PDP ke shirin fuskantar zabuka a Ekiti da Osun, har zuwa zaben 2027.



