Wasu tsoffin jami’an rundunar ’yan sandan Nijeriya sun sake kira ga rundunar da ta bi hukuncin Kotun Kwadago ta Kasa, wadda ta bayar da umarnin a mayar da su bakin aiki bayan an yi musu ritaya ba bisa ka’ida ba. Jami’an, da ke cikin rukuni na kwasa-kwasan horaswa na 33, 34 da 35, sun ce an yi musu ritaya ne tun kafin su cika wa’adin shekaru 35 da doka ta tanada.
Kotun, karkashin Mai shari’a Oyewumi Oyebiola, ta umurci Sufeton Janar na ’Yan Sanda, Hukumar Kula da Ayyukan ’Yan Sanda da Sakataren Rundunar su mayar da jami’an bakin aiki, tare da hana tilasta musu ritaya. Sai dai duk da hukuncin da aka yanke tun ranar 19 ga Afrilun 2022, har yanzu ba a aiwatar da umarnin kotun ba.
A wata wasika da lauyansu, Adetoye Adejola, ya rubuta wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, jami’an sun roki shugaban Nijeriya ya shiga tsakani domin tabbatar da bin hukuncin kotu. Sun ce kin aiwatar da hukuncin na ci gaba da tauye hakkinsu tare da barazana ga tsarin shari’a da kuma tsaron cikin gida na ƙasa.



