Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA
Jaridar Daily Trust ta ce attajirin na Afirka, Dangote, ya yi haka ne bayan da wata hukumar gwamnatin Nijeriya ta fara duba wadannan zarge-zarge na facaka da dukiyar kasa da ya yi wa wannan tsohon babban jami’in hukumar da ke da ruwa da tsaki kan sha’anin man fetur.
Sai dai ICPC ta jaddada cewa wannan mataki ba zai dakatar da binciken da take yi ba.



