Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa an kammala dukkan matakai tsaruka domin biyan alawus-alawus na wasannin Super Eagles a gasar AFCON 2025, inda ta ce ‘yan wasan za su fara ganin kuɗaɗen a asusunsu kafin ranar Juma’a.
A wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, 8 ga Janairu, 2026, karamar Ministar kuɗi,Doris Uzoka-Anite, ta ce za a biya kuɗaɗen zai a asusun ‘yan wasa na ƙasashen waje tun daga Alhamis din nan zuwa Juma’a.
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan wasan Super Eagles sun yi barazanar ƙin tafiya zuwa birnin da za a buga wasan daf da na kusa da na ƙarshe,sakamakon rashin biyan alawus-alawus ɗin da suke bi.



