DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wasu ‘yan Jam’iyyar APC sun nemi Tinubu da ya sauke ministan Abuja Nyesom Wike daga mukaminsa

-

Wasu shugabanni a jam’iyyar APC, ƙarƙashin APC Leaders Forum da Tinubu/Shettima Solidarity Movement, sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta cire Nyesom Wike daga muƙamin ministan Abuja, bisa zargin rashin biyayya, ayyukan da suka sabawa da kuma barazana ga haɗin kan ƙasa.

A cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 7 ga Janairu, 2026, wadda aka aike wa Shugaba Tinubu ta hannun shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ƙungiyoyin sun ce halayen Wike ba su dace da ci gaba da zama a matsayin minista ba.

Google search engine

An mika wasiƙar ne a ranar Laraba, yayin da mambobin ƙungiyoyin suka gudanar da zanga-zangar lumana a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Abuja, inda suka ce manufarsu ita ce kare martabar jam’iyya, dimokuraɗiyya da kuma ajandar gwamnatin Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara