Wasu shugabanni a jam’iyyar APC, ƙarƙashin APC Leaders Forum da Tinubu/Shettima Solidarity Movement, sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta cire Nyesom Wike daga muƙamin ministan Abuja, bisa zargin rashin biyayya, ayyukan da suka sabawa da kuma barazana ga haɗin kan ƙasa.
A cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 7 ga Janairu, 2026, wadda aka aike wa Shugaba Tinubu ta hannun shugaban APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ƙungiyoyin sun ce halayen Wike ba su dace da ci gaba da zama a matsayin minista ba.
An mika wasiƙar ne a ranar Laraba, yayin da mambobin ƙungiyoyin suka gudanar da zanga-zangar lumana a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Abuja, inda suka ce manufarsu ita ce kare martabar jam’iyya, dimokuraɗiyya da kuma ajandar gwamnatin Tinubu.



