DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu na hasashen samun saukin hauhawar farashi a Nijeriya cikin 2026

-

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi hasashen cewa hauhawar farashin kayayyaki a kasar zai sauka kasa da kashi 10 cikin 100 a shekarar 2026, lamarin da ya ce zai taimaka wajen inganta rayuwar ‘yan kasa da kuma kara habakar tattalin arziki (GDP).

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da mai ba Shugaba Tinubu shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar ranar Juma’a, 9 ga Janairu 2026, yayin da Shugaba Tinubu ke yaba wa kamfanonin Nijeriya da masu ruwa da tsaki a kasuwar zuba hannun jari bisa samun Naira tiriliyan 100.

Google search engine

Shugaban ya ce cimma wannan matsayi alamar tattalin arzikin Nijeriya na ci gaba da farfadowa ne, inda ya bukaci ‘yan kasa da ‘yan kasuwa su kara zuba jari a Nijeriya, yana mai tabbatar da cewa shekarar 2026 za ta fi alfanu ga masu zuba jari sakamakon ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren tattalin arzikin gwamnatinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara