DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriya 408,000 ne ke gudun hijra a Nijar, Kamaru da Chadi ta dalilin matsalolin tsaro in ji MDD

-

Fiye da ‘yan Nijeriya 408,000 ne ke ci gaba da gudun hijira a kasashen Nijar, Kamaru da Chadi, sakamakon matsalar rashin tsaro da ya addabi yankin Arewa maso Gabashin ƙasar tun shekarar 2009, a cewar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya UNHCR.

Rahoton UNHCR na shekarar 2025 ya bayyana cewa Jamhuriyar Nijar ce ke dauke da mafi yawan ‘yan Nijeriya da ke gudun hijira a can, inda ake da mutane 258,653, yawancinsu na zaune a yankin Diffa, kusa da kananan hukumomi kamar Kuluk, Gashua, Machina da Malkotan.

Google search engine

Kasashen Kamaru na dauke da ‘yan gudun hijira 126,892, mafi yawansu na sansanin Minawao da ke yankin Far North, yayin da Chadi ke dauke da mutane 21,636, musamman a yankin Lac Province da Baga Sola.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara