DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Trump ya yi sabuwar barazanar kara kawo sabbin hare-hare a Nijeriya

-

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake yin barazanar sake kai hare-haren a Nijeriya idan aka ci gaba da kashe Kiristoci, duk da musanta wa da gwamnatin Nijeriya.

Trump, ya bayyana cewa Amurka na iya kara kai hare-haren soji a Nijeriya idan aka ci gaba da kashe Kiristoci a kasar, kamar yadda jaridar New York Times ta rawaito a wata hira da aka wallafa ranar Alhamis, 8 ga Janairu 2026.

Google search engine

Kamfanin dillancin labarai na Reuters,ya rawaito cewa Trump ya yi wannan jawabi ne yayin da ake tambayarsa kan harin soji da Amurka ta kai Nijeriya a ranar Kirsimeti, inda sojojin Amurka suka ce sun kai harin ne kan ‘yan kungiyar IS a yankin Arewa maso Yammacin Nijeriya bisa bukatar gwamnatin Nijeriya.

Trump ya kara da cewa duk da cewa Musulmi ma ana kashe su a Nijeriya, a cewarsa Kiristoci ne suka fi fuskantar hare-hare, ra’ayin da gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da shi, tana mai jaddada cewa ‘yan ta’adda na kashe Musulmi da Kiristoci baki daya, ba tare da nuna wariya ta addini ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara