DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mutumin da ake zargi da aikata assha da diyarsa a jihar Bauchi

-

Rundunar ’yan sandan jihar Bauchi ta kama wani mutum mai shekaru 28 bisa zargin lalata da ’yarsa ta cikinsa ’yar shekara takwas, lamarin da ya faru a ƙaramar hukumar Alkaleri ta jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar ranar Alhamis, an ce wanda ake zargin ya kira yarinyar zuwa bandaki, inda ake zargin ya aikata laifin a kanta ba tare da amincewarta ba.

Google search engine

An ce an kai rahoton lamarin ofishin ’yan sanda ranar 31 ga Disamba, 2025,bayan karɓar rahoton, tawagar bincike ƙarƙashin jagorancin CSP Kadiri Danjuma, DPO na Alkaleri, ta gaggauta zuwa wurin, ta kai yarinyar asibiti domin duba lafiyarta, sannan ta kama wanda ake zargin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara