DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mutumin da ake zargi da aikata assha da diyarsa a jihar Bauchi

-

Rundunar ’yan sandan jihar Bauchi ta kama wani mutum mai shekaru 28 bisa zargin lalata da ’yarsa ta cikinsa ’yar shekara takwas, lamarin da ya faru a ƙaramar hukumar Alkaleri ta jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar ranar Alhamis, an ce wanda ake zargin ya kira yarinyar zuwa bandaki, inda ake zargin ya aikata laifin a kanta ba tare da amincewarta ba.

Google search engine

An ce an kai rahoton lamarin ofishin ’yan sanda ranar 31 ga Disamba, 2025,bayan karɓar rahoton, tawagar bincike ƙarƙashin jagorancin CSP Kadiri Danjuma, DPO na Alkaleri, ta gaggauta zuwa wurin, ta kai yarinyar asibiti domin duba lafiyarta, sannan ta kama wanda ake zargin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara