DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Trump ya dauki matakin hana kwace kudaden Venezuela daga asusun Amurka

-

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya rattaba hannu kan wani umarni na musamman ‘Executice Order’ da ke nufin hana kotuna ko masu bin bashi kwace kudaden shiga daga sayar da man fetur na Venezuela da ke cikin asusun Ma’aikatar Kuɗi ta Amurka, in ji Fadar White House.

 

Google search engine

Umarnin dai ya yi nuni da cewa matakin zai taimaka wa kasar Venezuela wajen samar da tsaro, zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

 

Wannan ya zo ne kasa da mako guda bayan da sojojin Amurka suka kutsa birnin Caracas tare da yin awon gaba da shugaban Venezuela Nicolas Maduro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara