DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iran ta shiga rana ta huɗu da katse intanet yayin da ake ci gaba da zanga-zanga

-

An shiga rana ta huɗu da gwamnatin ƙasar Iran ke ci gaba da katse intanet a faɗin ƙasar, a daidai lokacin da ake ci gaba da zanga-zangar adawa da ake cewa ita ce mafi girma a Iran cikin sama da shekaru uku.

Kamar yadda gidan talabijin na Channels TV ya ruwaito, ƙungiyar sa ido kan harkokin intanet ta NetBlocks ta bayyana cewa zuwa safiyar Litinin, katsewar intanet ɗin ta kai sama da sa’o’i 84 ba tare da yankewa ba.

Google search engine

Rahotanni sun nuna cewa katsewar na zuwa ne a lokacin da dubban ’yan ƙasar ke ci gaba da fitowa kan tituna domin nuna adawa da manufofin gwamnati, duk da ƙoƙarin da hukumomi ke yi na takaita sadarwa da yada labarai.

Masu sa ido na kasa da kasa na bayyana damuwa cewa katse intanet na iya ƙara ta’azzara take haƙƙin bil’adama, tare da hana duniya samun cikakken bayani kan abin da ke faruwa a Iran a halin yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara