’Yan bindiga da ke tsakanin jihohin Kano da Katsina sun kakaba haraji ga manoma har ₦50,000 a kowace eka ga manoma, musamman masu noman rake, kafin su girbe amfanin gonarsu.
Jaridar The Guardian ta bayyana cewa ’yan bindigar sun kafa sansanoni a Dajin Rugu da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina da kuma Dajin Falgore a karamar hukumar Doguwa a jihar Kano, inda suke karɓar haraji da yi wa manoman barazana.
Rahoton ya nuna cewa manoman da suka ƙi biyan harajin na fuskantar barazana, lalata amfanin gona, da yiwuwar kai musu hari, lamarin da ya tilasta wa da dama barin gonakinsu,kuma yawanci manoman rake ne suka fi fuskantar wannan matsala.



