DCL Hausa Radio
Kaitsaye

WHO ta bukaci gwamnatoci su kara haraji kan lemuka da giya

-

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta yi kira ga gwamnatocin duniya da su kara haraji sosai kan lemun zaki da kuma barasa, tana mai cewa hakan na da muhimmanci wajen rage mace-mace da cututtuka. WHO ta ce wadannan abubuwan sha suna saukin samu kuma farashinsu ya yi kasa a kasashe da dama, lamarin da ke kara yawaitar kiba, ciwon sukari, cutar daji da raunuka.

Daraktan Janar na WHO, Dr. Tedros Ghebreyesus, ya bayyana hakan yayin wani taro ta yanar gizo a ranar Talata, inda ya ce harajin lafiya na taimakawa wajen rage amfani da kayayyakin da ke cutar da lafiya, tare da rage nauyi a kan tsarin kiwon lafiya. Ya kara da cewa kudin da ake samu daga harajin na ba gwamnatoci damar saka hannun jari a fannin lafiya, ilimi da walwalar jama’a.

Google search engine

Rahoton WHO ya nuna cewa a kalla kasashe 116 sun riga sun kakaba haraji kan lemun zaki, amma wasu kayayyaki kamar ruwan ‘ya’yan itatuwa kashi 100 cikin 100, madarar da aka zuba sukari, da shayin kofi da ake sayarwa a shirye, na tsallake harajin. Haka kuma, rahoton ya ce kasashe 167 na karbar haraji kan barasa, amma farashinsa ya cigaba da sauki tun daga 2022 saboda rashin daidaita haraji da hauhawar farashi da kudin shiga kamar yadda Punch ta ruwaito.

WHO ta jaddada cewa yawan shan lemun zaki na da alaka da kiba, ciwon sukari na nau’i na biyu, cututtukan zuciya da matsalolin hakora, yayin da barasa ke kara hadarin cututtuka ga uwa da jariri, lalacewar lafiyar kwakwalwa da yawaitar hatsari. Hukumar ta kawo misalin Birtaniya, inda aka kakaba haraji kan lemun zaki a 2018, lamarin da ya rage yawan sukari da ake sha, ya samar da fam miliyan 338 a 2024, tare da rage kiba a tsakanin ‘yan mata masu shekaru 10 zuwa 11, musamman a yankunan talakawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara