DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Jihar Sokoto ta yi karin haske kan bidiyon mazauna kauyen Tidibale da ƴan bindiga suka kora daga gidajensu

-

Gwamnatin Jihar Sokoto ta ce mutanen da aka gani a wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, ’yan garin Tidibale ne a Karamar Hukumar Isa, amma ba ’yan bindiga suka kore su ba, kamar yadda ake yadawa.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulɗa da Jama’a na Fadar Gwamnati, Abubakar Bawa, ya fitar a ranar Alhamis 15 ga Janairu, 2026, inda ya ce an ɗauki matakin kwashe mutanen ne na ɗan lokaci bayan samun jita-jitar cewa ’yan bindiga na shirin kai hari yankin.

Google search engine

Sanarwar ta ce kansilan mazabar Tidibale, Dayyabu Sani, ne ya kai rahoton jita-jitar ga Shugaban Karamar Hukumar Isa, Alhaji Sherifu Kamarawa, wanda daga nan ya bayar da umarnin kwashe mutanen zuwa hedkwatar karamar hukumar a matsayin matakin kariya. Daga bisani, an mayar da mutanen lafiya zuwa gidajensu, yayin da jami’an tsaro suka ƙara sintiri a yankin.

Gwamnatin Jihar Sokoto ta kuma sanar da amincewa da kafa sansanin sojoji na Forward Operations Base (FOB) a Tidibale domin ƙarfafa tsaro, tare da gargadin jama’a kan yaɗa jita-jita da siyasantar da batutuwan tsaro.

Hakazalika, ta kuma bukaci ’yan ƙasa da su haɗa kai da hukumomi wajen yaki da ’yan bindiga, tare da tona asirin masu bai wa miyagu bayanai a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara