DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kashim Shettima ya jagoranci sakin tsuntsaye a bikin ranar tunawa da sojoji ta 2026

-

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya jagoranci manyan jami’an gwamnati wajen sakin tsuntsaye a bikin Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026, a matsayin alamar kudirin Nijeriya na zaman lafiya, hadin kai da ’yanci.

An gudanar da bikin ne tare da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio; Babbar Alkalin Alkalan Nijeriya, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun; Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, da sauran manyan baki. An wallafa bidiyon taron ne a ranar Alhamis ta hannun Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Nijeriya kan Harkokin Watsa Labarai (Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), Stanley Nkwocha.

Google search engine

Tsuntsayen da aka saki sun tashi nan take, abin da masu kallo suka bayyana a matsayin alama ta kimar sadaukarwa da jaruman sojojin Nijeriya da suka rasu suka bayar domin kare kasa.

Ana gudanar da Ranar Tunawa da Sojoji a ranar 15 ga Janairu duk shekara, domin girmama ’yan rundunar sojin Nijeriya da suka sadaukar da rayuwarsu a bakin aiki, ciki har da Yakin Basasa, ayyukan wanzar da zaman lafiya, da kuma yaki da ’yan ta’adda da masu tayar da kayar baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara