DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dokokin harajin Tinubu za su kare martabar masu karamin karfi a Nijeriya – Taiwo Oyedele

-

Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Gyaran Tsarin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa kananan masu zuba jari a kasuwar hannayen jari ba su da alhakin biyan harajin ribar jari, yana mai cewa dokar haraji ta 2026 ta fi mayar da hankali ne kan kare masu karamin karfi da kara kudin hannun jama’a.

Oyedele ya fadi haka ne a taron Cowry Quarterly Economic Discourse, inda ya ce dokar ta ba da cikakken rangwame ga duk wanda kudin da ya samu daga sayar da kadarori bai wuce Naira miliyan 150 ba, kuma ribar ba ta haura Naira miliyan 10 cikin watanni 12, ba tare da wani sharadi ba.

Google search engine

Ya kara da cewa manyan masu kudi ne kawai ke biyan harajin idan sun fice daga zuba jari gaba daya ba tare da sake zuba kudin ba, yayin da kudin da aka sake zubawa ke samun rangwame. Ya ce wannan tsarin yana karfafa ci gaban kasuwar jari da bunkasar tattalin arziki.

Oyedele ya kuma bayyana cewa dokar haraji ta 2026 ta kawo karshen “harajin talauci,” inda ya ce ma’aikatan da ke karbar mafi karancin albashi ba sa biyan harajin shiga kwata-kwata, tare da kara ka’idar cewa masu karfin biyan haraji su fi daukar nauyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara