Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Gyaran Tsarin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa kananan masu zuba jari a kasuwar hannayen jari ba su da alhakin biyan harajin ribar jari, yana mai cewa dokar haraji ta 2026 ta fi mayar da hankali ne kan kare masu karamin karfi da kara kudin hannun jama’a.
Oyedele ya fadi haka ne a taron Cowry Quarterly Economic Discourse, inda ya ce dokar ta ba da cikakken rangwame ga duk wanda kudin da ya samu daga sayar da kadarori bai wuce Naira miliyan 150 ba, kuma ribar ba ta haura Naira miliyan 10 cikin watanni 12, ba tare da wani sharadi ba.
Ya kara da cewa manyan masu kudi ne kawai ke biyan harajin idan sun fice daga zuba jari gaba daya ba tare da sake zuba kudin ba, yayin da kudin da aka sake zubawa ke samun rangwame. Ya ce wannan tsarin yana karfafa ci gaban kasuwar jari da bunkasar tattalin arziki.
Oyedele ya kuma bayyana cewa dokar haraji ta 2026 ta kawo karshen “harajin talauci,” inda ya ce ma’aikatan da ke karbar mafi karancin albashi ba sa biyan harajin shiga kwata-kwata, tare da kara ka’idar cewa masu karfin biyan haraji su fi daukar nauyi.



