DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu tattalin arzikin Nijeriya na girgidi, bai tsaya da kafafunsa ba in ji bankin duniya da IMF

-

Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) sun bukaci Gwamnatin Tarayya da sauran hukumomi su dauki tsauraran matakai domin rage hauhawar farashi, duk da cewa ana samun wasu ci gaba a bangaren tattalin arziki a Nijeriya.

Manyan jami’an biyu, wato Babban Masanin Tattalin Arziki na Bankin Duniya a Nijeriya, Dokta Samer Matta, da Wakilin IMF a Nijeriya, Dokta Christian Ebeke, sun bayyana haka ne a Legas yayin taron NESG na hasashen tattalin arziki na 2026. Sun amince cewa gyare-gyaren tattalin arziki na haifar da ci gaba, amma sun jaddada cewa hauhawar farashi har yanzu na da yawa.

Google search engine

Dokta Ebeke ya gargadi Nijeriya kan yin sakaci da tunanin cewa a riga an kammala aiki, yana mai cewa komawa tsoma bakin gwamnati wajen daidaita farashi da kasuwa ba zai dore ba. Ya bukaci gwamnatocin tarayya da jihohi su tabbatar da ingancin kashe kudade domin amfanin ya isa ga rayuwar talakawa.

A nasa bangaren, Dokta Matta ya ce kodayake hauhawar farashi na raguwa, har yanzu babbar barazana ce ga jin dadin al’umma. Ya bukaci a mayar da hankali kan kashe kudi a bangaren jin dadin jama’a, musamman ilimi, lafiya da kariyar zamantakewa, yana mai cewa jihohi na da karin kudade kuma dole su yi amfani da su yadda ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara