DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba harin ‘yan bindiga ba ne — rikicin CJTF da tsoffin ‘yan bindiga ya yi sanadiyyar rasa rai a kauyen jihar Katsina – ‘Yan sanda

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta musanta rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Tuge inda suka harbe tare da jikkata mazauna yankin.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa abin da ya faru ba harin ‘yan bindiga ba ne, illa rikici da ya barke tsakanin wasu mambobin Civilian Joint Task Force (CJTF) da kuma wasu da ake zargin tsoffin ‘yan bindiga ne ‘yan asalin kauyen Tuge Mai Zuri da ke karamar hukumar Musawa a jihar Katsina.

Google search engine

A cewar DSP Abubakar Sadiq Aliyu, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, lamarin ya faru ne da misalin karfe 9:35 na safiyar Asabar, 17 ga Janairu, 2026, lokacin da rikici ya kaure tsakanin bangarorin biyu, har aka yi musayar wuta. Hakan ya janyo jikkatar mutane hudu sakamakon harsasan da aka harba inda daya daga cikinsu ya rasu bayan an kai shi asibiti, yayin da sauran uku ke karbar magani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara