DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindigar da suka sace Kiristoci 166 a Kaduna sun nemi kafin alkalamin N29m

-

Barayin dajin da suka sace Kiristoci 166 a jihar Kaduna sun nemi N29m matsayin ‘kafin-alkalami’ kafin su fadi adadin kudin fansar da za a biya.

Rahotanni sun tabbatar da cewa a ranar Lahadi 18 ga watan Janairun 2026, ‘yan bindiga sun kutsa cikin majami’u uku a yankin Kurmi Wali da ke kudancin Kaduna tare da sace masu ibadar.

Google search engine

Tun da fari dai gwamnatin jihar Kaduna ta musanta batun, kafin daga bisani ta tabbatar da faruwar lamarin.

A halin yanzu al’ummar yankin da aka sace mutanen sun tsinci kawunan su cikin firgici, inda da dama suka tsere daga muhallansu tare da dakatar da sauran harkoki, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Adams Oshiomhole ya buƙaci gwamnatin Tinubu ta garƙame duk wanda ya ƙi biyan haraji

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

‘Yan APC kawai jam’iyyar za ta ba mukamai bayan zaben 2027 – Nentawe Yilwatda

Shugaban jam'iyyar APC na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda ya bayyana cewa ba za su bai wa duk wanda ba dan jam’iyya mukami ba bayan zaben...

Mafi Shahara