DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriya sama da dubu 13 da suka makale aka dawo da su gida daga kasashen waje a cikin shekaru 3 – Rahoton jaridar Punch

-

Akalla ‘yan Nijeriya 13,635 da suka makale a kasashen waje aka dawo da su gida daga kasashe 10 cikin shekaru uku da suka gabata, kamar yadda bayanai daga Hukumar IOM, NEMA da NiDCOM suka nuna.

An dawo da mutanen ne daga Libya, Sudan, Saudiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Ghana, Jamhuriyar Nijar, Aljeriya, Chadi, Côte d’Ivoire da Mali.

Google search engine

A shekarar 2025 kadai, an dawo da ‘yan Nijeriya 3,358 daga kasashe biyar, inda aka fi dawo da su daga Libya (1,773) da Jamhuriyar Nijar (1,188). A 2024 kuma, an kwaso mutane 4,261 daga kasashe bakwai, ciki har da Libya, Nijar, Chadi, Mali da UAE, yayin da a 2023 aka dawo da 5,753 galibi daga Sudan, Libya da Nijar.

Gwamnatin Nijeriya ta sake gargadin matasa da su guji yin hijira ba bisa ka’ida ba, musamman bin tayin ayyukan bogi a kasashen waje. Ma’aikatar Harkokin Waje da Ma’aikatar Matasa sun ce hijira bisa doka tana da amfani, amma wadda ba ta bi ka’ida ba na jefa rayuka cikin hadari tare da illata ci gaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara