DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwamishina a gwamnatin Abba a Kano ya ajiye mukaminsa

-

Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire na Jihar Kano, Yusuf Ibrahim Kofarmata, ya yi murabus daga mukaminsa nan take, yana danganta matakin da yanayin rikicin siyasa da ke gudana a jihar.

A cikin wasikar murabus dinsa, Kofarmata ya ce yanayin siyasar da ke cike da matsin lamba da tsammanin biyayya na iya kawo shakku kan ‘yancin yanke hukunci da tsarkin aikinsa a matsayin kwamishina, abin da ya ce bai dace da ka’idojin aiki na gwamnati ba.

Google search engine

Ya ce ya dauki matakin ne domin kare martabar mukamin da kuma amincewar jama’a, inda ya gode wa Gwamnatin Jihar Kano bisa damar da aka ba shi, yana fatan murabus dinsa zai taimaka wa ma’aikatar ta cigaba da aiki ba tare da tangarda ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara