DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun hallaka ‘yan bindiga 3 tare da ceto wasu a wasu kauyukan iyakokin jihar Gombe

-

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta tabbatar da hallaka wasu ‘yan bindiga uku tare da kwato makamai da harsasai, sannan ta ceto wasu daga cikin mutanen da aka sace a wani samame da aka gudanar a yankunan kan iyakar jihar.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce jami’an tsaro sun dakile yunkurin hari a yankunan Pindiga, Billiri da Shongom ranar Juma’a, amma ‘yan bindigar sun kai hari Garin Galadima da ke yankin Lambo da misalin karfe 3 na asubahin Asabar, inda suka yi ajalin mutum daya tare da sace biyar.

Google search engine

Ya ce biyo bayan farmakin, ‘yan sanda da mafarauta sun fafata da ‘yan bindigar, lamarin da ya yi sanadin hallak uku lahira daga cikinsu, kwato bindigogin AK-47 guda biyu, harsasai 120, babura hudu, da kuma ceto mutane uku, yayin da rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran da suka tsere.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara