Hukumar Kula da ayyukan ‘yansandan Nijeriya (PSC) tare da rundunar ‘yansandan sun tsawaita wa’adin ɗaukar sabbin ‘constable’ guda 50,000 da makonni biyu, bayan da aka samu ƙarancin masu nema daga wasu jihohi ciki har da Legas.
A ranar 26 ga Nuwamban 2025, Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro a faɗin ƙasar, inda ya umarci rundunar ‘yansanda da sojojin ƙasa su ɗauki ƙarin jami’ai domin tunkarar ta’azzarar matsalar tsaro.
An buɗe shafin yin rijistar neman aikin a ranar 15 ga Disambar 2025, kuma an tsara rufewa a ranar 25 ga Janairun 2026.
Sai dai a cewar wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na PSC, Mista Torty Kalu ya fitar a ranar Litinin yanzu an tsawaita wa’adin zuwa ranar 8 ga Fabrairun 2026.



