DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar ‘yansandan Nijeriya ta tsawaita wa’adin daukar jami’ai aiki

-

Hukumar Kula da ayyukan ‘yansandan Nijeriya (PSC) tare da rundunar ‘yansandan sun tsawaita wa’adin ɗaukar sabbin ‘constable’ guda 50,000 da makonni biyu, bayan da aka samu ƙarancin masu nema daga wasu jihohi ciki har da Legas.

 

Google search engine

A ranar 26 ga Nuwamban 2025, Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro a faɗin ƙasar, inda ya umarci rundunar ‘yansanda da sojojin ƙasa su ɗauki ƙarin jami’ai domin tunkarar ta’azzarar matsalar tsaro.

 

An buɗe shafin yin rijistar neman aikin a ranar 15 ga Disambar 2025, kuma an tsara rufewa a ranar 25 ga Janairun 2026.

 

Sai dai a cewar wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na PSC, Mista Torty Kalu ya fitar a ranar Litinin yanzu an tsawaita wa’adin zuwa ranar 8 ga Fabrairun 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara