Jagoran al’ummar kauyen Jamigbe a mazabar Gawu da ke yankin Abaji a Abuja, Mai Martaba Alhaji Danladi Aliyu, ya tabbatar da rasa ran wani malami mai suna Usman Mohammed sakamakon saran maciji.
Lamarin da ya faru a makarantar firamare ta yankin, ya jefa fargaba a cikin zukatan iyaye, dalibai da malamai baki daya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Da ya ke jawabi, Alhaji Danladi ya ce mamacin ya gamu da ajalinsa ne, bayan da macijin ya shiga ofishinsa ta cikin wani rami ya kuma buya a karkashin kujera.
Bayan saran malamin, rahotanni sun nuna cewa macijin ya yi masa tsartuwa a idanunsa, inda jim kadan da mika shi asibiti likitoci suka tabbatar da rasuwar sa.
Alhaji Danladi ya dora alhakin faruwar lamarin da lalacewar makarantar da yayi sanadiyar bai wa halittu kamar maciji damar shiga ciki.




Innalillahi wa’inna Ilaihirraji’un, Ubangiji Allah ya gafarta masa