Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bar filin sauka da tashin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe domin Kai ziyarar aiki kasar Turkiyya da kuma karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
Sanarwar da fadar gwamnati ta fitar, ta ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa a muhimman bangarori da suka hada da tsaro, ilimi, ci-gaban al’umma, kirkire-kirkire, harkokin sufurin jiragen sama, sadarwa, kasuwanci, da kuma zuba jari.
Kazalika wannan ziyara ta biyo bayan ziyarar da Shugaba Recep Tayyip Erdoğan na Turkiyya ya kai Nijeriya a tsakanin 19 da 20 ga Oktoban 2021, wadda ta ƙara dankon alaƙa tsakanin Abuja da Ankara.



