DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojin Amurka sun bayyana ƙara tallafi don inganta tsaron Nijeriya

-

Rundunar sojin Amurka ta ce ta na ƙara tura kayan aikin soja tare da faɗaɗa raba bayanan sirri da Nijeriya, a wani ɓangare na ƙoƙarin Amurka na ƙara haɗin gwiwa da rundunonin sojin Afirka domin fatattakar ’yan bindigar da ke addabar nahiyar.

 

Google search engine

Mataimakin kwamandan rundunar sojin Amurka a Afirka, Laftanar Janar John Brennan, wanda ya bayyana hakan yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na AFP, ya ƙara da cewa Ma’aikatar Tsaron Amurka (Pentagon) ta ci gaba da buɗe hanyoyin sadarwa da rundunonin soji a ƙasashen Sahel da ke ƙarƙashin mulkin soja, ciki har da Burkina Faso, Nijar da Mali, duk da sauye-sauyen siyasa da suka faru a yankin.

 

Wannan ya zo ne bayan harin da Amurka ta kaddamar a Nijeriya kan ‘yan ta’adda, lamarin da ya haifar da cece-kuce, duk da cewa gwamnatin Nijeriya ta kare matakin da cewa akwai sahalewar ta, kana kuma ta bayar da bayanan sirri ga Amurkan kafin kaddamar da harin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara