DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta karyata rade-radin sauya Shettima a takarar Tinubu 2027

-

Jam’iyyar APC ta musanta rahotannin da ke cewa ana shirin sauya Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takarar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a zaɓen 2027.

 

Google search engine

Sakataren Yaɗa Labarai na APC na Ƙasa, Felix Morka, ne ya yi wannan bayani a shirin Politics Today na Channels a ranar Litinin, inda ya ce rade-radin ba su da tushe.

 

“Yin hasashe kan sunayen mutanen da za su maye gurbin Mataimakin Shugaban Ƙasa kuskure ne. Bisa Dokar Zaɓe da dokokin ƙasa, an hana duk wasu harkokin kamfe yanzu. Bai kamata mu riƙa tattauna wannan batu sosai ba, yadda kafafen watsa labarai da jama’a ke yi.” In ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara