DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta karyata rade-radin sauya Shettima a takarar Tinubu 2027

-

Jam’iyyar APC ta musanta rahotannin da ke cewa ana shirin sauya Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takarar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a zaɓen 2027.

 

Google search engine

Sakataren Yaɗa Labarai na APC na Ƙasa, Felix Morka, ne ya yi wannan bayani a shirin Politics Today na Channels a ranar Litinin, inda ya ce rade-radin ba su da tushe.

 

“Yin hasashe kan sunayen mutanen da za su maye gurbin Mataimakin Shugaban Ƙasa kuskure ne. Bisa Dokar Zaɓe da dokokin ƙasa, an hana duk wasu harkokin kamfe yanzu. Bai kamata mu riƙa tattauna wannan batu sosai ba, yadda kafafen watsa labarai da jama’a ke yi.” In ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka biya kudin fansa, aka karbi kudin aka kuma ki sako mutanen a...

Dattawan al’ummar Gidan Waya da ke ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna sun bayyana cewa sun sayar da buhunan masara sama da 3,000 domin tara...

Sojoji sun amince an kitsa yunkurin juyin mulki kan Tinubu

Rundunar sojin Najeriya ta amince cewa wasu jami’anta sun kitsa yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne...

Mafi Shahara