DCL Hausa Radio
Kaitsaye

China ta yi alkawarin tallafa wa Cuba bayan barazanar Amurka

-

Gwamnatin China ta sha alwashin tallafa wa kasar Cuba bayan da Amurka ta yi mata barazana.

Gwamnatin Trump dai ta umarci Cuba da ta dauki matakin kulla yarjejeniya da ita, ko kuma ta fuskanci irin halin da Venezuela ta tsinci kanta a ciki.

Google search engine

A kwanakin baya sojojin Amurka sun kutsa cikin birnin Caracas tare da yin awon gaba da shugaban Venezuela Nicolas Maduro.

Sai dai mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China Guo Jiakun ya yi tir da lamarin, tare da bayyana cikakken goyon baya ga Cuba, kamar yadda ta saba yi a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara