DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci ma’aikatan Abuja su dakatar da yajin aikin da suke yi

-

Mai shari’a Emmanuel Subilim na kotun ma’aikata ta Nijeriya ya bai wa daukacin ma’aikatan Abuja da ke yajin aiki umarnin su dakatar har zuwa lokacin da za a sake zaman sauraron shari’ar.

 

Google search engine

Wannan umarni ya biyo bayan karar da ministan Abuja Nyesom Wike ya shigar gaban kotun, yana neman ta tilasta wa ma’aikatan komawa bakin aiki.

 

A cewar mai shari’ar, wajibi ne a dakatar da duk wani sabani aka mika shi gaban kotu, har sai ta kammala aikinta, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya wallafa.

 

Kazalika ya ce duk wanda aka samu da kin bin umarni ko sabawa doka tabbas zai fuskanci hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara