Ma’aikata kamfanonin da ke yin giya za su yi zanga-zanga muddin ba a janye umarnin haramta amfani da barasar leda a Nijeriya ba.
Ma’aikatan sun bayyana haka ne yayin da suka yi fitar dango zuwa ofishin hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta Nijeriya NAFDAC da ke Legas.
A cewar su, matakin na shafar ayyukansu na yau da kullum musamman ta bangaren samun kudaden shiga, tare da cewa zai shafi akalla ‘yan Nijeriya miliyan 5.
Tuni dai shugabar hukumar NAFDAC Farfesa Mojisola Adeyeye ta tattauna da wadanda suka jagoranci zanga-zangar, amma ta ce ba za a dage haramcin ba har sai an samu sauye-sauye daga bangaren majalisar dokokin Nijeriya.



