DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘National Grid’ ya sake faduwa karo na biyu a 2026

-

Rumbun wutar lantarki na Nijeriya ya sake faduwa a karo na biyu cikin wannan shekarar ta 2026 a ranar Talata.

 

Google search engine

Kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito, bayanai sun nuna cewa a lokacin haɗa rahoton, babu ko megawatt ɗaya da ake samarwa ga kamfanonin rarraba wuta 11 na ƙasar.

 

Wannan na zuwa ne bayan da grid ɗin ya fuskanci faduwa karo na farko a bana a ranar Juma’a da ta gabata, wanda kuma ya zo makonni kaɗan bayan irin wannan matsala a ranar 29 ga Disamba, 2025.

 

Har zuwa lokacin da aka kammala rahoton, Hukumar Rarraba Wutar Lantarki ta Nijeriya (TCN) ba ta fitar da cikakken bayani kan abin da ya jawo wannan matsala ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara