Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF ta dakatar da kocin Senegal, Pape Thiaw, wasanni guda biyar tare da cinsa tarar dala $100,000, bisa zargin aikata rashin da’a a yayin wasan ƙarshe na gasar kofin Afrika AFCON, da aka buga tsakanin Senegal da Morocco.
Rahotanni daga CAF sun nuna cewa an dauki matakin ne bayan da Thiaw ya umurci ‘yan wasansa su fice daga fili yayin wasan karshe da Morocco, abin da hukumar ta bayyana a matsayin saba wa dokokin wasanni da cin mutuncin gasar.



