DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Real Madrid za ta kara da Benfica yayin da PSG za ta fafata da Monaco a wasan neman shiga zagaye na 16 na kofin nahiyar Turai

-

An fitar da jadawalin wasannin gurbin shiga zagaye na 16 na gasar UEFA Champions League, inda Real Madrid za ta kara da Benfica, yayin da Paris Saint-Germain za ta fafata da Monaco, bayan kammala fitar kuri’a a birnin Nyon na kasar Switzerland.

Wasannin sun haifar da manyan fafatawa, ciki har da Borussia Dortmund da Atalanta, Galatasaray da Juventus, Atlético Madrid da Club Brugge, Olympiacos da Bayer Leverkusen, yayin da Qarabağ za ta hadu da Newcastle United karon farko a tarihi. Inter Milan kuma za ta buga da Bodø/Glimt ta Norway.

Google search engine

Karawar Benfica da Real Madrid ta kara daukar hankali ne bayan Benfica ta doke Madrid 4–2 a karshen wasannin league phase a ranar 28 ga Janairu 2026, lamarin da ya sa Madrid ta fadi zuwa matakin play-off maimakon shiga zagaye na 16 kai tsaye.

UEFA ta bayyana sabon tsarin gasar a matsayin mai cike da kayatarwa, inda aka ce wasannin sun yi matukar daukar hankali. Za a buga wasannin play-off din ne kafin a tantance kungiyoyin da za su shiga zagaye na 16, yayin da wasan karshe zai gudana a birnin Budapest.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hatsari ya yi ajalin mutum 5,289 a Nijeriya cikin 2025 – Hukumar FRSC

Hukumar kiyaye hadurra ta Nijeriya, FRSC, ta bayyana cewa an samu hatsarin mota 10,446 a fadin kasar a shekarar 2025, inda mutane 5,289 suka rasa...

Majalisa Dattawa ta nemi Tinubu ya kafa sansanin soji a Katsina bisa dawowar hare haren ‘yan bindiga a jihar

Majalisar Dattawan Nijeriya ta nuna matuƙar damuwa kan tabarbarewar tsaro a jihar Katsina, musamman a yankin Funtua, bayan hare-haren ’yan bindiga da suka yi sanadin...

Mafi Shahara